Connect with us

Firstpost

Saudiyya ta ƙaƙaba wa masu laifukan rashin ɗa’a sabuwar tara

Saudiyya ta ƙaƙaba wa masu laifukan rashin ɗa’a sabuwar tara

Gwamnatin Saudiyya ta sanar da sanya tarar kuɗi kan masu aikata ayyukan da suka shafi rashin ɗa’a a cikin al’umma, musamman a lokutan salla, domin kare mutunci, tsaro da kuma zaman lafiya.

Sabbin matakan, wanda za a fara aiwatarwa nan take, sun shafi masu sanya kaya marasa mutunci a bainar jama’a, da masu kunna kiɗa lokacin salla, da masu bahaya ko zubar da shara a wuraren da doka ta haramta.

A cewar sabuwar doka, duk wanda aka kama da kunna kiɗa a lokacin salla zai biya tara ta Riyal 1,000 (kimanin Naira 390,000) a karon farko, kuma idan aka sake kama shi, tarar za ta ninka zuwa Riyal 2,000 (kimanin Naira 780,000).

Haka kuma, duk wanda ya sa tufafi marasa mutunci a bainar jama’a za a ci shi tara ta Riyal 100, sannan idan ya sake maimaitawa tarar za ta ƙaru zuwa Riyal 500.

An kuma haramta zubar da shara ko bahaya a wuraren da doka ta hana. Kuma duk wanda ya karya wannan doka a karon farko zai biya Riyal 500, sannan a karo na biyu tarar za ta ninka zuwa Riyal 1,000.

Bugu da ƙari, duk wanda aka kama yana ɗaukar hoto ko bidiyo ba tare da izini ba, za a ci shi tara ta Riyal 1,000, sannan idan ya maimaita laifin tarar za ta ninka zuwa Riyal 2,000.

Sabbin dokokin na Saudiyya na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnati ke ƙoƙarin ƙara tsaurara matakan ladabtar da jama’a, musamman a wuraren ibada da jama’ar musulmi ke taruwa.

Continue Reading
You may also like...

More in

Recent Post

Advertisement Enter ad code here

Facebook

Headlines

To Top